Isa ga babban shafi
cote d'Ivoire

Yaya da Kolo Toure zasu kauracewa Manchester City

Kasar Cote d’iVoire ta yi watsi da bukatar Manchester city game da tsaikun gayyatar ‘yan uwan juna Yaya Toure da kolo Toure domin dawowa gida buga gasar cin kofin Afrika da za’a gudanar a cikin watan nan.

Yaya Touré lokacin da yake karbar kyautar gwarzon Afrika a kasar Ghana.
Yaya Touré lokacin da yake karbar kyautar gwarzon Afrika a kasar Ghana. AFP PHOTO / GLO / Temmanuel Quaye
Talla

Yanzu haka kuma ‘Yan wasan biyu ba dasu Manchester city zata buga wasan FA ba, da zata fafata tskaninta da Manchester United a ranar lahadi. Bayan kocin Cote d’Ivoire ya bukaci ‘yan wasan.

A ranar Assabar ne ‘yan wasan guda biyu zasu hadu a birnin Paris na Faransa daga nan kuma su tashi zuwa Abu Dhabi inda zasu kwashe tsawon makwanni biyu suna horo kafin mikawa zuwa Gabon da Equatorial Guinea.

Kocin Cote d’Ivoire Francois Zahoui ya fitar da jerin ‘yan wasa 25 da zasu haska a gasar, da suka hada da Didier Zokora da ke taka kwallo a kungiyar Trabzonspor ta kasar Turkiya da Emmanuel Eboue na Galatasaray, hadi da Salomon Kalou Chelsea da Didier Drogba da Gervinho Arsenal a Ingila.
 

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.