Kai-tsaye
RFI kai-tsaye
Saurari dukannin labaran RFI kai-tsaye a shafinmu na yanar gizo Ana iya samun RFI a cikin harshen Faransanci
Saurara kai-tsaye
Kundayen labarai na sauti
-
Rayuwata
Yadda matsin rayuwa ya shafi zawarawa sakamakon a Najeriya
A yau shirin RAYUWATA ya duba halin da zaurawa ke ciki a daidai lokacin nan da ake fama da matsananciyar tsadar rayuwa a Najeriya, wanda ake alakantawa da janye tallafin man fetur da shugaban Kasar Bola Ahmed Tinubu ya yi Jim kaɗan bayan rantsar da shi a cikin shekarar da ta gabata.02/10/2024 10:00 -
Tambaya da Amsa
Alfanun siyasar Birtaniya ga kasashen Afrika,ko yaya zaben su ke gudana?
A cikin shirin tambaya da amsa, a duk karshen mako,Nasiru Sani kan kawo maku wasu daga cikin amshoshin ku masu saurare.A wannan mako za ku ji amsa dangane da siyasar Birtaniya,da wasu daga cikin amsoshin tambayoyin ku masu saurare.28/09/2024 19:50 -
Mu Zagaya Duniya
Yadda babban taron zauren Majalisar Ɗinkin Duniya ya gudana
Daga cikin labarun da shirin Mu Zagaya Duniya na wannan makon ya waiwaya, akwai yadda babban taron zauren Majalisar Ɗinkin Duniya ya gudana, haka nan akwai bitar rahoton maƙudan ƙuɗaɗen da ECOWAS ta ware don samar da wutar lantarki a makarantu da cibiyoyin kiwon lafiya, a wasu ƙasashen da ke ƙarƙashinta ciki har da Najeriya, haka nan shirin ya waiwari halin da ake ciki game da rikicin Isra'ila da Hezbollah a Lebanon.28/09/2024 20:00 -
Bakonmu a Yau
Yusuf Tuggar a kan Najeriya da kujerar dindindin a kwamitin Tsaro MDD
Kamar yadda wata kila kuka ji a cikin labaran duniya, Ministan harkokin wajen Najeriya, Ambassada Yusuf Tuggar ya bayyana manyan dalilan da ya kamata a yi dubi da su domin sanya kasar a matsayin mambar kwamitin tsaro na Majalisar Dinkin Duniya. Shugaban Sashen Hausa na RFI, Mr Joseph Penney ya tattauna da ministan a zauren Majalisar dake ci gaba da gudanar da taronta a New York ta kasar Amurka, kuma ga yadda zantawarsu ta gudana.27/09/2024 03:30 -
Bakonmu a Yau
Hukumar GIABA ta shirya taron fadakar da 'yan kasuwa da masu masana'antu da kuma lauyoyi
Hukumar yaki da cin hanci da rashawa ta kasashen Afirka ta Yamma, wato GIABA ta shirya wani taron fadakar da 'yan kasuwa da masu masana'antu da kuma lauyoyi a kan hakkin da ya rataya a kansu na kin bada dama ga masu halarta kudaden haramun ko kuma 'yan ta'adad su yi amfani da su wajen boye kudaden sata. Taron na kwanaki 2 na gudana ne a birnin Lagos. Bashir Ibrahim Idris ya tattauna da mai magana da yawun GIABA Mr Timothy Melaye, kuma ga yadda zantawarsu ta gudana.26/09/2024 03:19 -
Rayuwata
Gwamnatin jihar Filato ta kafa dokar ɗakile cin zarafin mata, yara
Cin zarafin mata da kananan yara guda ne daga cikin batutuwan da gwamnatoci da kungiyoyi masu zaman kansu ke kara kaimi akai wajan yaki da faruwar hakan, sai dai ta wani fannin a iya cewa ana maganin kaba ne kai na kunburi,domin kuwa kara samun yawaitar hakan ake a cikin al’umma.A wannan rana shirin yayi duba ne kan yadda yawaitar cin zarafin mata da kananan yara a jihar Plateau dake Najeriya ta sanya gwamnatin jihar yin doka ta musamman, domin yi wa tufkar hanci.25/09/2024 09:59 -
Kasuwanci
Najeriya: Yadda ambaliyar ruwa ta kassara tattalin arzikin al'ummar Maiduduri
Shirin 'Kasuwa A kai Miki Dole' na wannan makon tare da Ahmed Abba ya leka ne jihar Barno da ke arewa maso gabashin Najeriya, inda ya mayar da hankali kan tasarin tattalin arziki da ambaliyar baya-bayan nan ya haifarwa jihar da ma al'ummarta.25/09/2024 10:23 -
Bakonmu a Yau
Dokta Abdulhakim Garba Funtua kan hare-haren Isra'ila a Lebanon
Kasashen duniya sun fara mayar da martani dangane da kazamin hare haren da Isra'ila ke kai wa a yankin kudancin Lebanon wanda a jiya kawai ya kai ga hallaka mutane kusan 300. Cikin wadanda suka bayyana damuwa da yadda yakin Isra'ilar ke fadada har da Sakatare Janar na Majalisar dinkin duniya Antonio Guterres. Dangane da wannan yaki Bashir Ibrahim Idris ya tattauna da Dr Abdulhakeem Garba Funtua na Babbar Kwalejin Fasaha dake Kaduna, kuma ga yadda zantawarsu ta gudana.24/09/2024 03:35