Kungiyoyin fararen hula a tarayyar Najeriya sun bukaci Ministan kudin kasar Ngozi Nwela Okonjo yin murabus daga mukaminta, sakamakon zarginta wajen yin ruwa da tsaki ga karin farashin Man Fetur a kasar.A tattaunawar shi da Muhammad Salisou Hamisou, Dr. Hussaini Abdu na kungiyar Action aid yace gwamnatin Jonathan ta dogara ne da Ngozi domin ita ce bokan gwamnatin saboda shugaban bai san komi ba game da ci gaban tattalin arzikin kasar.
Sauran kashi-kashi
-
Hare haren Iran a kan Isra'ila ya dada fadada yakin dake gudana a Gabas ta Tsakiya- Dr Abbati
Hare haren da kasar Iran ta kaddamar a kan Isra'ila ya dada fadada yakin dake gudana a Gabas ta Tsakiya, tun bayan kazamin harin da mayakan Hamas suka kaddamar a kan yahudawa ranar 7 ga watan Oktobar bara.Martanin da Isra'ila ta mayar ya yi sanadiyar kai hare hare a yankunan Falasdinawa da Yemen,Lebanon,Syria da kuma Iran abinda ya yi sanadiyar hallaka mutane sama da dubu 40.Bashir Ibrahim Idris ya tattauna da Dr Abbati Bako, mai sharhi a kan siyasar duniya, kuma ga yadda zantawarsu ta gudana03/10/202403:33 -
Yusuf Tuggar a kan Najeriya da kujerar dindindin a kwamitin Tsaro MDD
Kamar yadda wata kila kuka ji a cikin labaran duniya, Ministan harkokin wajen Najeriya, Ambassada Yusuf Tuggar ya bayyana manyan dalilan da ya kamata a yi dubi da su domin sanya kasar a matsayin mambar kwamitin tsaro na Majalisar Dinkin Duniya. Shugaban Sashen Hausa na RFI, Mr Joseph Penney ya tattauna da ministan a zauren Majalisar dake ci gaba da gudanar da taronta a New York ta kasar Amurka, kuma ga yadda zantawarsu ta gudana.27/09/202403:30 -
Hukumar GIABA ta shirya taron fadakar da 'yan kasuwa da masu masana'antu da kuma lauyoyi
Hukumar yaki da cin hanci da rashawa ta kasashen Afirka ta Yamma, wato GIABA ta shirya wani taron fadakar da 'yan kasuwa da masu masana'antu da kuma lauyoyi a kan hakkin da ya rataya a kansu na kin bada dama ga masu halarta kudaden haramun ko kuma 'yan ta'adad su yi amfani da su wajen boye kudaden sata. Taron na kwanaki 2 na gudana ne a birnin Lagos. Bashir Ibrahim Idris ya tattauna da mai magana da yawun GIABA Mr Timothy Melaye, kuma ga yadda zantawarsu ta gudana.26/09/202403:19 -
Dokta Abdulhakim Garba Funtua kan hare-haren Isra'ila a Lebanon
Kasashen duniya sun fara mayar da martani dangane da kazamin hare haren da Isra'ila ke kai wa a yankin kudancin Lebanon wanda a jiya kawai ya kai ga hallaka mutane kusan 300. Cikin wadanda suka bayyana damuwa da yadda yakin Isra'ilar ke fadada har da Sakatare Janar na Majalisar dinkin duniya Antonio Guterres. Dangane da wannan yaki Bashir Ibrahim Idris ya tattauna da Dr Abdulhakeem Garba Funtua na Babbar Kwalejin Fasaha dake Kaduna, kuma ga yadda zantawarsu ta gudana.24/09/202403:35 -
Ambasada Abubakar Chika kan fara taron Majalisar Ɗinkin Duniya
Yau ake fara taron babban zauren Majalisar dinkin duniya karo na 79, wanda ake saran ya gudanar da mahawara a kan batutuwa da dama cikin su harda sabon daftarin majalisar wanda ya kunshi sauyin yanayi da rikice rikice da matsalar sauyin yanayi da rashin shugabanci na gari tare da matsalar yunwa. Dangane da wannan taro Bashir Ibrahim Idris ya tattauna da Ambasada Abubakar Chika, tsohon jakadan Najeriya a kasar Iran, kuma ga yadda zantawarsu ta gudana.23/09/202403:33